DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dalilin da ya sa har yanzu Shugaba Tinubu bai dawo gida ba – Fadar shugaban kasa

-

Fadar shugaban Nijeriya ta mayar da martani kan sukar da ake yi wa Shugaba Tinubu, yayin da yake ci gaba da zama a kasar waje a dai dai lokacin da kasar ke fuskantar kalubale da dama.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Bayo Onanuga ya fitar, ya ce shugaban yana ci gaba da gudanar cikin harkokin mulkin Najeriya duk da cewa yana Turai, kuma yana sa ido sosai kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya.

Ya kara da cewa shugaban zai dawo Abuja domin ci gaba da aikinsa bayan hutun Esther.

Duk da cewa fadar shugaban kasa ta ce shugaba Tinubu na ziyarar aiki ne a kasar a hukumance, sai dai rahotanni sun ce ya gana da mai bai wa Trump shawara kan harkokin tattalin arziki da tsaro.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara