Ministan babban birnin Abuja Nyesom Wike, ya goyi bayan matakin ayyana dokar ta-baci a jihar Ribas, da Shugaban Bola Tinubu yana mai cewa ya so a tsige gwamna Siminalayi Fubara a matsayin gwamnan jihar.
Matakin dakatar da Fubara, da mataimakiyarsa Ngozi Odu da ‘yan majalisar dokokin kasar na tsawon watanni a jihar Ribas saboda rikicin siyasa, na ci gaba da janyo muhawara.
Sai dai Wike, a wata fira da yan jarida, ya ce matakin da shugaban kasar ya dauka ya kamar ceton Rivers, yana mai cewa matakin nada gwamnan rikon kwarya shine abinda ya dace