DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa Stanley Nkwocha

-

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana Kashim shettima shiga ofishin shugaban kasa a matsayin labari mara tushe bare makama,face son batawa fadar shugaban kasa suna.

Sanarwar Stanley dai ta rawaito cewa an ta yada labarin cewa akwai wani sojoji da aka girke suka hana mataimakin shugaban kasa Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa.

Sanarwa ta kara da cewa ba wani sabon abu bane, domin kuwa ko a farkon wannan makon, an ta yada hotunan allunan yekuwar yakin neman zaben Shugaba Tinubu da Kasshim wanda tuni Fadar Shugaban Kasar ta fito karara ta musanta.

Stanley Nkwocha ya kuma kara da cewa, Mataimakin shugaban kasar ya ci gaba da maida hankali kan ayyukansa,da kuma marawa shugaban kasa baya wajen cimma muradun ‘yan Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara