DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

-

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a zaben 2027 mai zuwa.

Duk da cewa har yanzu Shugaba Tinubu bai kai rabin wa’adinsa na farko ba, kuma bai bayyana aniyarsa ta sake tsayawa takara a hukumance ba, amma shugabannin jam’iyyar APC sun yi amfani da dandalin taron hadin kan babban birnin tarayya Abuja—wanda aka gudanar a filin wasa na Old Parade da ke Abuja, domin nuna goyon bayansu ga takararsa karo na biyu.

An shirya taron ne domin tarbar shugaban karamar hukumar Abuja Municipal Area Council (AMAC) Hon. Christopher Zakka Maikalagu, kansiloli, da dubban magoya bayansu sun shigo jam’iyyar APC daga jam’iyyar adawa ta PDP.Da yake zantawa da manema labarai a wajen taron, mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau I. Jibrin maliya, ya bayyana kwarin gwiwar sake zaben Tinubu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara