DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

-

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu da jam’iyyar APC a 2027, yana mai bayyana hakan a matsayin bata lokaci.

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, wanda ya kasance dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a 2023 da kuma tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, wanda kwanan nan ya sauya sheka zuwa jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) daga APC ne ke jagorantar gamayyar.

Sai dai tsohon gwamnan na jihar Ekiti yana ganin hadakar za ta gaza ne saboda gwamnonin jam’iyyar PDP ba sa tare da Atiku, domin suna fafutukar kare kansu a siyasance, kamar yadda ya bayyana acikin shirin siyasa a tashar talabijin ta channels.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara