Karancin wutar lantarki da aka samu a Kano cikin kwanaki 10 da suka gabata ya kawo cikas ga harkokin zamantakewa da tattalin arziki a cikin babban birnin.
Wasu mazauna Kano da suka zanta da manema labarai, sun koka da cewa lamarin da suka ce ya gurgunta musu harkokin yau da kullum.
Wani mai walda a unguwar Dakata a karamar hukumar Nasarawa, Abubakar Bala, ya ce dogaro da man diesel don ci gaba da gudanar da sana’arsa ba zai dore ba.