Mukaddashin shugaban jam’iyyar PDP a jihar Ribas, Robinson Ewor ya zargi shugaba Bola Tinubu da bai wa ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, kudade domin ruguza jam’iyyar adawa ta PDP.
A yayin wata hira da gidan Talabijin na Arise a ranar Litinin, Ewor ya bayyana cewa Wike ba dan jam’iyyar PDP ne na gaskiya ba.
Ya yi mamakin abin da ya hana ministan Abuja Nyesom Wike ficewa daga PDP, domin a cewarsa yanzu APC yake yi wa aiki.