DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Neja ta sa dokar hana zirga-zirgar ababen hawa a Minna babban birnin jihar saboda matsalar tsaro

-

Gwamnan jihar Neja, Umaru Mohammed Bago, ya sanya dokar hana fita daga karfe 6 na yamma zuwa 6 na safe a Minna babban birnin jihar, sakamakon yawaitar hare-hare dake ajalin mutane da dama a birnin.

A cewar gwamnan yanzu haka an takaita zirga-zirgar babura da masu tuka keke tsakanin karfe shida na yamma zuwa karfe shida na safe.

Bago ya bayyana hakan ne a yayin wani taro kan tsaro da masu ruwa da tsaki da suka hada da sarakunan gargajiya da shugabannin hukumomin tsaro wanda ya gudana a gidan gwamnati a Talatar nan.

Sai dai sanarwar ta ce wannan matakin bai shafi fita saboda lalura ta rashin lafiya ba.

Ya bayyana cewa sabon matakin na da nufin dakile matsalolin tsaro da ke kara tabarbarewa a babban birnin jihar.

Gwamnan ya jaddada cewa gwamnati ba za ta zauna a yayin da masu aikata laifuka ke ci gaba da kai hare-hare da ajalin mutanen da ba su ji ba ba su gani ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara