DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin tarayya ta jaddada kudirinta na magance matsalar rashin tsaro da ke addabar kasar

-

Mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Malam Nuhu Ribadu, ya bayar da wannan tabbacin ne a ranar Talata a ziyarar da ya kai Makurdi, babban birnin jihar Benue, domin jajanta wa al’ummar jihar kan asarar rayukan da aka yi a baya-bayan nan.

Da yake zantawa da manema labarai, Ribadu ya bayyana cewa gwamnatin shugaba Tinubu ta gaji matsalar tsaro, wanda hakan ke zama babbar barazana ga zaman lafiyar kasa, amma duk da haka an fara shawo kan matsalar.

A cewarsa, matsalar rashin tsaro da kasar ke fuskanta ta faro ne kimanin shekaru 15 da suka gabata kuma ya jaddada cewa ba ta da nasaba da siyasa, addini ko kabilanci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara