DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar NAHCON ta saka ranar da maniyyata aikin hajjin Nijeriya na 2025 za su fara tashi zuwa Saudiyya

-

Hukumar alhazai ta kasa NAHCON a cikin wata sanarwa da mataimakiyar daraktan yada labaran hukumar Fatima Sanda Usara ta fitar, ta tunatar da shugabannin hukumomin jin dadin alhazai na jihohi cewa hukumar na yin shiri na karshe kafin a fara jigilar mahajjata daga ranar ranar 22 ga watan Afrilu 2025.

Shugaban hukumar Farfesa Abdullah Saleh Usman wanda ya gana sakatarorin hukumomin, ya yi kira ga shugabannin da su ci gaba da wayar da kan alhazai wajen yin rigakafi tare da tabbatar da yin duk wasu abubuwa da ake bukata.

A yayin taron an bayyana cewa jirgin Air Peace zai dauki alhazai 5,128 daga jihohin Abia, Akwa Ibom, Anambra, Bayelsa, Benue, Borno, Cross River Delta, Ebonyi, Edo, Ekiti, Enugu, Imo, Kogi, Ondo, Rivers, Taraba da Taraba.

Sai kuma kamfanin FlyNas an ware masa maniyyata 12,506 daga Abuja, Kebbi, Lagos, Ogun, Osun, Sokoto da Zamfara, yayin da kamfanin Max Air zai yi jigilar alhazai daga jihohin Bauchi, Gombe, Jigawa, Kano, Katsina, Kwara, Oyo da Plateau.

Kamfanin Umza kuwa zai yi jigilar maniyyata 10,163 daga jihohin Kaduna, Adamawa, Nasarawa, Neja da Yobe.

Sanarwar ta ce kusan alhazai 43,000 ne za su sauka a kasa mai tsarki domin yin ibadar aikin hajjin shekarar 2025.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara