Daruruwan magoya bayan gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Siminalayi Fubara, sun fito fito yin zanga-zanga a ranar Talata, inda suke neman a mayar da shi kan kujerarsa.
Masu gangamin dai suna sanye da bakaken kaya ɗauke da kwalayen masu rubutun kin amincewa da sauke Fubara.
Ba wannan ne karon farko ba da ake zanga-zangar kin jinin gwamnatin Tinubu, tun lokacin da shugaban kasa Bola Tinubu ya ayyana dokar ta-baci a jihar tare da dakatar da Fubara, mataimakiyarsa, Ngozi Odu, da ‘yan majalisar dokokin jihar.