Fasinjojin da ke filin tashi da saukar jiragen sama na Murtala Muhammed da ke Legas da filin jirgin Nnamdi Azikiwe da ke Abuja, sun nuna damuwa kan matakin da ma’aikatan hukumar hasashen yanayi ta Najeriya na fara yajin aikin sai baba ta gani a fadin kasar daga daren ranar Talata.
Yayin da wasu fasinjojin ke cikin rudani game da lokacin da za a fara yajin aikin, da dama sun fara kokawa game da yiyuwar dakatar da tashin wasu jiragen saman, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito
Ma’aikatan sun shirya zanga-zangar ne, saboda zargin hukumar ta NiMet da gaza aiwatar da mafi karancin albashi, rashin biyan alawus din ma’aikata, da yin watsi da bukatar shigar da ma’aikatan da aka cire a tsarin albashi a baya, da dai sauransu.