DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Akwai yiyuwar samun tsaikon tashin jiragen sama saboda yajin aikin da ma’aikatan hukumar hasashen yanayi suka shiga a Nijeriya

-

Fasinjojin da ke filin tashi da saukar jiragen sama na Murtala Muhammed da ke Legas da filin jirgin Nnamdi Azikiwe da ke Abuja, sun nuna damuwa kan matakin da ma’aikatan hukumar hasashen yanayi ta Najeriya na fara yajin aikin sai baba ta gani a fadin kasar daga daren ranar Talata.

Yayin da wasu fasinjojin ke cikin rudani game da lokacin da za a fara yajin aikin, da dama sun fara kokawa game da yiyuwar dakatar da tashin wasu jiragen saman, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito

Ma’aikatan sun shirya zanga-zangar ne, saboda zargin hukumar ta NiMet da gaza aiwatar da mafi karancin albashi, rashin biyan alawus din ma’aikata, da yin watsi da bukatar shigar da ma’aikatan da aka cire a tsarin albashi a baya, da dai sauransu.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara