DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An tsare wasu jami’an hukumar Civil Defence bisa zargin tatsar kudade a hannun jama’a da suka kai Naira miliyan 5.2

-

Hukumar tsaro ta farin kaya ta Nijeriya ta bayar da umarnin tsare wasu jami’an da ake zargin suna da hannu wajen karbar naira miliyan 5.2 daga hannun wani matafiyi, biyo bayan umarnin da ministan harkokin cikin gida, Dr. Olubunmi Tunji-Ojo ya bayar.

Umurnin na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai magana da yawun hukumar NSCDC, Afolabi Babawale, a ranar Laraba.

Lamarin wanda ya dauki hankulan jama’a a shafukan sada zumunta, an ruwaito jami’an na karbar kudin ne daga hannun wani matashi da ya taso daga Ado-Ekiti a jihar Ekiti zuwa Akure, jihar Ondo.

A matakin da ya dauka, kwamandan rundunar, Ahmed Audi, ya yi Allah wadai da halayyar da jami’an suka nuna, abin da ya bayyana rashin da’a da kuma saba wa ka’idar aiki da hukumar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara