Shugaban hukumar Kwastam ta Najeriya Adewale Adeniyi, ya ce al’adar fasa kwaurin mai na ci gaba da yaɗuwa ne saboda bambancin farashin man fetur tsakanin Najeriya da kasashen da ke makwabtaka da ita.
Da yake jawabi yayin taron bitar watanni uku na farkon 2025 da hukumar ta gudanar a Abuja ranar Talata, Adeniyi ya lura cewa duk da cire tallafin man fetur, hakan bai hana masu fasa-kwauri fitar da mai daga Najeriya ba bisa ka’ida ba.
Shugaban na Kwastam ya jaddada cewa, gagarumin gibin farashin na ci gaba da kara yawaitar fasa-kwauri.