Gwamnatin tarayya ta ayyana filin jirgin saman Bola Ahmed Tinubu, dake Minna jihar Neja a matsayin madadin filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe na Abuja.
Ministan Sufurin Jiragen Sama Festus Keyamo ne ya bayyana haka a wajen ƙaddamar da tashi da saukar jiragen sama a filin jirgin saman Bola Ahmed Tinubu, inda jirgin sama na Overland Airways ya fara tashi.
Keyamo ya ce filin jirgin yana da tsari da yanayin da ya dace da kowane filin jirgin sama na kasa da kasa a fadin duniya, kuma za a rika amfani da shi a duk lokacin da aka samu cunkoson jirage ko wata matsala a filin jirgin sama na Abuja.