Hukumar Hisbah a jihar Kano ta rushe wani wuri da ke a Dakata cikin kwaryar birnin, bayan bazuwar jita-jita cewa wurin na dauke da sawun kafa na fiyayyen halitta Annabi Muhammad SAW.
Majiyar DCL Hausa ta jaridar Daily Trust ta ba da labarin cewa, wurin, da a kwana nan aka share domin gina layin dogo, ya ja hankalin dumbin mabiya addinin Musulunci bayan bayyanar wata alamar sawun kafa a cikin laka, tare da fitar ruwa daga wurin.
Jita-jitar da ta yadu cikin gaggawa cewa “Ruwan Albarka” na bubbuga a wurin kuma yana dauke da sawun Annabi, lamarin da ya sa mutane ke zuwa domin neman waraka da samun tubarraki.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Mataimakin Kwamandan Hisbah na jihar Kano, Dr Mujahideen Aminudeen, ya gargadin jama’a da kada su yarda da irin wadannan labaran da ke jefa mutane a hanyar bata.