Sabuwar kungiyar ta’addanci mai suna Mahmuda ta zafafa kai hare-hare ga wasu al’ummomi a jihohin Kwara da Neja.
Wasu da ake zargin ‘yan sabuwar kungiyar ta’adda ta Mahmuda ne, sun kai hari a kananan hukumomin Ilesha Baruba, Kemaanji, Baruten da Kaiama na jihar Kwara a daren Lahadi.
A ranar Juma’a ne aka ruwaito cewa yan ta’addan sun kashe wasu ‘yan banga a jihar, kamar yadda jaridar Dailytrust ta ruwaito.