DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dakatattun ‘yan majalisar dokokin Zamfara sun ja daga tare da nada wani shugaban majalisa

-

‘Yan majalisar dokokin jihar Zamfara guda tara da aka dakatar, sun yi wani zaman majalisar dokoki tare da zabar sabon kakakin majalisa, lamarin da ke nuni da ruruwar wutar rikicin siyasar jihar.

‘Yan majalisar, wadanda aka dakatar a watan Fabrairun 2024 bisa zarginsu da rashin da’a, sun yi wani zama na farko a wani wuri da ba a bayyana ba a ranar Laraba, a cewar jaridar Dailytrust.

Yayin zaman sun zabi Hon. Bashir Aliyu Gummi a matsayin shugaba, haka kuma sun umurci Gwamna Dauda Lawal da ya sake gabatar da kudurin kasafin kudin shekarar 2025 a gaban majalisar ta su.

Mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar Adamu Aliyu ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici, inda ya jaddada bukatar daukar matakin ladabtarwa.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara