DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An ji karar harbe-harbe a wurin taron magoya bayan Wike a jihar Bayelsa

-

An shiga cikin tashin hankali a birnin Yenagoa ta jihar Bayelsa, bisa karar harbe-harbe da aka ji a wurin masu biyayya ga ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike karkashin wata kungiya mai suna NEW Associates.

Kungiyar ta shirya taron ne karkashin jagorancin George Turnah, jigo a jam’iyyar PDP a jihar.

Ana ci gaba da gudanar da taron ne a lokacin da aka yi ta jin karar harbe-harbe a yankin, kamar yadda jaridar Dailytrust ta ruwaito.

Da yake yi wa manema labarai jawabi bayan harbe-harbe, sakataren kungiyar NEW Associates a jihar Bayelsa, Comrade Ebilade Ekerefe, ya ce za su ci gaba da gudanar da taron.

A halin yanzu, magoya bayan NEW Associates sun sake haduwa don ci gaba da gangamin taron.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara