DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ka yi watsi da kiraye-kirayen komawa jam’iyyar PDP – kira ga Peter Obi

-

Mataimakin shugaban jam’iyyar Labour Party na kasa, Dr Ayo Olorunfemi, ya shawarci tsohon dan takarar shugaban kasa Peter Obi da ya yi watsi da duk kiraye-kirayen ficewa daga jam’iyyar gabanin babban zaben 2027.

Olorunfemi, wanda shi ne dan takarar jam’iyyar LP a zaben gwamnan jihar Ondo a 2024, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Nijeriya ranar Lahadi a Legas cewa ya kamata Obi ya mayar da hankali wajen sake gina jam’iyyar.

Olorunfemi, wanda ya bayyana cewa duk da cewa Obi na da ‘yanci shiga duk jam’iyyar da yake so, ya ce yana bukatar ya yi hattara sosai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara