DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

-

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya.

Bafarawa, wanda ya kasance jigo a jam’iyyar babbar jam’iyyar adawa ta PDP har zuwa ranar 13 ga Janairun 2025, ya sanar da murabus dinsa daga jam’iyyar, yana mai bayyana cewa yana son mayar da hankali kan shirye-shiryen bunkasa matasa.

Kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito, tsohon gwamnan jihar Sokoto ya ce ’yan siyasar Najeriya sun fi mayar da hankali ne wajen samun mukaman siyasa ba tare da yin wani abu na amfani ga al’umma ba.

Bafarawa ya yi wannan jawabi ne a yayin da wasu fitattun ’yan adawa ke sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki, a shirye-shiryen da ake yi gabanin zaben 2027.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara