DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Obi ba ya bukatar hadaka da PDP ko kawance da Atiku don kayar da Tinubu – NLC

-

Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) ta bayyana cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party a zaben 2023, Peter Obi, baya bukatar haɗin kan jam’iyyar PDP ko wasu jiga-jigan siyasa irinsu Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da Nasiru El-rufa’I domin samun nasara a zaben 2027.

Wannan jawabi ya fito daga bakin Mataimakin shugaban kungiyar ta ƙasa, Farfesa Theophilus Ndubuaku, a wata hira ta musamman. Ya ce Peter Obi na da farin jini a tsakanin al’umma, kuma shi ne mutum mafi cancanta da zai iya gaba-da gaba a kokarin kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a babban zaben da ke tafe.

Farfesa Ndubuaku ya kuma ƙaryata jita-jitar da ke yawo kan cewa Peter Obi zai koma jam’iyyar PDP, yana mai cewa PDP ta zama jam’iyyar da ke cike da rikice-rikice da rudani a kan sahihancin manufarta.

Ya jaddada cewa Peter Obi da jam’iyyar Labour za su tsaya tsayin daka wajen gina sabon tsari mai inganci a siyasar Najeriya, ba tare da dogaro da tsofaffin tsari na raunanan jam’iyyu ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara