DCL Hausa Radio
Kaitsaye

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

-

Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin jam’iyyar sun shirya wani muhimmin taro a ranar 11 ga watan Mayu, domin tunkarar kalubalen da ke barazana ga makomar jam’iyyar, musamman abun da ya shafi yawaitar sauya shekar da ke ci gaba da addabar jam’iyyar.

Wani amintaccen mamba daga cikin kwamitin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ne ya tabbatar wa jaridar PUNCH cewa shugabannin jam’iyyar da gwamnonin PDP za su gana a ranar 11 ga watan Mayu domin tattauna matsalolin da ke damun jam’iyyar.

Majiyar ta bayyana cewa taron zai fi mayar da hankali ne kan tsara dabarun dakile ci gaba da ficewar wasu jiga-jigan ‘ya’yan jam’iyyar, da warware matsalar da ta shafi kujerar Sakataren Jam’iyyar na Kasa, da kuma wasu muhimman batutuwa da ke ci gaba da addabar jam’iyyar a fadin kasar.

Ana kallon wannan taro a matsayin wani mataki na sake farfado da jam’iyyar tare da dunkulewa domin tinkarar zaben 2027 da ke tafe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara