DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Zaben Okowa a matsayin abokin takarar Atiku ne kuskuren da ya kayar da PDP a 2023 — Abba Moro

-

Shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa, Sanata Abba Moro, ya bayyana cewa zaɓen tsohon gwamnan jihar Delta, Ifeanyi Okowa, a matsayin abokin takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, babban kuskure ne da ya haifar da faduwar jam’iyyar.

Sanata Moro ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da Channels TV, inda ya mayar da martani kan kalaman Okowa da ya ce yana nadamar karɓar matsayin mataimakin Atiku. A cewar Sanata Moro, wannan furuci na Okowa bai dace ba, musamman da yake cewa shi da kansa ya nemi matsayin ba wani ya tilasta masa ba.

A cewarsa, akwai wasu fitattun ‘yan jam’iyyar PDP daga kudu da suka fi cancanta kuma da za su iya jawo ƙuri’u, idan aka zaɓe su maimakon Okowa. Ya kuma ce rashin samun nasara a jiharsa da kuma gaza kawo ƙuri’u daga Delta na nuna rashin karɓuwarsa a tsakanin jama’a.

Sanata Moro ya ƙara da cewa jam’iyyar PDP na da ƙwarin gwiwar sake dawowa da ƙarfin gwiwa gabanin zaɓen 2027, inda ya bayyana cewa shugabannin jam’iyyar daga jihohi 36 da Abuja, sun gana kwanan nan domin tsara yadda za a farfaɗo da jam’iyyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara