Kungiyar Arewa Consultative Forum (ACF) ta bayyana cewa yankin Arewa zai mara wa ɗan takara baya a zaɓen shugaban ƙasa na 2027 ne kawai idan ya nuna ƙwarin guiwar kare muradun yankin.
Shugaban kwamitin amintattu na kungiyar, Alhaji Bashir Dalhatu, ne ya bayyana hakan a ranar Laraba yayin wani taro da kungiyar ta gudanar a Kaduna, inda aka tattauna kan manyan matsalolin da ke addabar Arewa da ma kasa baki ɗaya.
Alhaji Dalhatu, wanda kuma shi ne tsohon Ministan Lantarki da Karfe, ya jaddada cewa ACF ba za ta goyi bayan kowanne ɗan takara ko jam’iyya ba sai dai waɗanda suka nuna cikakken kishin yankin Arewa da niyyar magance matsalolinsa da suka hada da rashin tsaro, talauci da koma bayan tattalin arziki.
Ya ce lokaci ya yi da Arewa za ta farka daga dogaro da alkawuran siyasa Mai kama da shificin gizo, tare da tabbatar da an zaɓi shugabanni masu gaskiya da rikon amana da za su kai yankin tudun mun tsira.