Hukumar ta ICPC da kan yaki cin hanci a tsakanin jami’an gwamnati wato ICPC ta bayyana cewa Naira biliyan 28.8 ne kawai aka rabawa dalibai a manyan makarantun gaba da sakandare maimakon Naira biliyan 100 da aka rabawa makarantun.
Hukumar ta ce binciken farko da ta gudanar ya gano cewa hukumomin jami’o’i daban-daban sun karkatar da adadin kudaden da basu kasa Naira biliyan 71.2 ba, kamar yadda jaridar Dailytrust ta ruwaito.
Kakakin hukumar, Demola Bakare, ya shaidawa manema labarai a Abuja cewa an gayyaci manyan masu ruwa da tsaki da suka hada da darakta janar na ofishin kasafin kudi da kuma akanta janar na kasa.
Haka kuma Bakare ya ce an gayyaci manyan jami’ai daga bankin CBN da kuma babban daraktan shirin bada lamuni na dalibbai wato NELFUND domin su ba da bayanai kan lamarin.