DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC

-

Hukumar ta ICPC da kan yaki cin hanci a tsakanin jami’an gwamnati wato ICPC ta bayyana cewa Naira biliyan 28.8 ne kawai aka rabawa dalibai a manyan makarantun gaba da sakandare maimakon Naira biliyan 100 da aka rabawa makarantun.

Hukumar ta ce binciken farko da ta gudanar ya gano cewa hukumomin jami’o’i daban-daban sun karkatar da adadin kudaden da basu kasa Naira biliyan 71.2 ba, kamar yadda jaridar Dailytrust ta ruwaito.

Kakakin hukumar, Demola Bakare, ya shaidawa manema labarai a Abuja cewa an gayyaci manyan masu ruwa da tsaki da suka hada da darakta janar na ofishin kasafin kudi da kuma akanta janar na kasa.

Haka kuma Bakare ya ce an gayyaci manyan jami’ai daga bankin CBN da kuma babban daraktan shirin bada lamuni na dalibbai wato NELFUND domin su ba da bayanai kan lamarin.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara