DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Badakalar da aka yi a gwamnatin Abba Gida Gida ta fi wadda aka yi a shekaru 8 na Ganduje – Tsohon sakataren gwamnatin Kano

-

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano Dr Abdullahi Baffa Bichi, ya yi kakkausar suka ga gwamnatin Abba Kabir Yusuf, inda ya zarge ta da yin almundahana da rashawa fiye da na gwamnatin da ta gabata.

A cikin wani faifan bidiyo, Bichi ya yi ikirarin cewa gwamnati mai ci ta tafka kurakurai fiye da lokacin tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, wanda a baya ake zarginsa da cin hanci da rashawa a tsawon mulkinsa na shekaru takwas, a cewar jaridar Dailytrust.

Bichi ya yi nuni da cewa gwamnatin ba za ta kai labari ba a zaben 2027, saboda korafin da ake yi kanta inda ya yi alkawarin fallasa aika-aikar da ake zargin gwamnatin da aikatawa.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara