DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Bankin raya Afirka ya kaddamar da shirin bayar da tallafin dala miliyan 650 ga Najeriya na tsawon shekaru 5

-

Bankin raya Afirka ya kaddamar da shirin bayar da tallafi na tsawon shekaru biyar ga Najeriya, inda zai rika samar da akalla dala miliyan 650 a kowacce shekara daga 2025 zuwa 2030 a wani yunkuri na kawo ci gaba ga tattalin arzikin kasar.

Kamar yadda wata sanarwa da bankin ya wallafa a shafinsa na yanar gizo ta nuna, shirin zai samar da dala biliyan 2.95 a shekaru hudun farko, yayin da za a karasa ragowar da adadin da yayi hasashen ya kai dala biliyan 3.21.

Kazalika sanarwar ta bayyana cewa shirin na da nufin cike gibin ayyukan ci gaba da Najeriya ke da shi, musamman inganta bangarorin da suka shafi ayyukan tituna, samar da wutar lantarki, samar da ruwan sha mai tsafta, da kuma samar da ayyukan yi sama ga mata da matasan kasar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara