Bankin raya Afirka ya kaddamar da shirin bayar da tallafi na tsawon shekaru biyar ga Najeriya, inda zai rika samar da akalla dala miliyan 650 a kowacce shekara daga 2025 zuwa 2030 a wani yunkuri na kawo ci gaba ga tattalin arzikin kasar.
Kamar yadda wata sanarwa da bankin ya wallafa a shafinsa na yanar gizo ta nuna, shirin zai samar da dala biliyan 2.95 a shekaru hudun farko, yayin da za a karasa ragowar da adadin da yayi hasashen ya kai dala biliyan 3.21.
Kazalika sanarwar ta bayyana cewa shirin na da nufin cike gibin ayyukan ci gaba da Najeriya ke da shi, musamman inganta bangarorin da suka shafi ayyukan tituna, samar da wutar lantarki, samar da ruwan sha mai tsafta, da kuma samar da ayyukan yi sama ga mata da matasan kasar.