DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An dage shari’ar zargin zamba kan tsohon minista Saleh Mamman saboda rashin tafinta-Daily Trust

-

An dage ci gaba da sauraron shari’ar Tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, da ake yi a gaban kotun Tarayya da ke Abuja, sakamakon rashin mai fassara wato tafinta a kotun.

A lokacin da aka kira shari’ar a ranar Juma’a, Lauyan masu gabatar da kara, Barrister A.O. Mohammed, ya shaida wa kotu cewa duk da cewa an shirye ci gaba da sauraron shari’a, yana fuskantar cikas na rashin mai fassara.

Ya bayyana cewa an shaida masa cewa mai fassarar kotu na bakin aiki a wani muhimman taro na da aka tura shi.

Saboda haka, Lauyan ya roki kotu da ta bayar da ɗan gajeren lokaci don samun damar kawo mai fassara gabanin cigaba da shari’ar.

Lauyan da ke kare wanda ake tuhuma, Barrister Emmanuel Hassan, bai yi jayayya da bukatar ba.

A sakamakon haka, Mai shari’a James Omotosho ya dage sauraron karar zuwa ranakun 8 da 9 ga Mayu domin ci gaba da shari’a.

Hukumar EFCC ce dai ke tuhumar Saleh Mamman da laifuka 12 da suka shafi hada baki da karkatar da kudade ta ba bisa ka’ida.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara