DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu inda aka yi son-rai wajen zaben jami’an da za su yi wa alhazai hidima a hajjin 2025 – NAHCON

-

Hukumar kula da hajji ta Nijeriya NAHCON ta nesanta kanta daga zargin cin hanci da rashawa a cikin tsarin zaben tawagar likitocin da za ta kula da masu aikin hajji na shekarar 2025.

Jaridar Daily Nigerian ta ba da labarin cewar ana zargin NAHCON da yin wata kumbiya-kumbiya wajen zaben ma’aikatan wucin gadi da za a tura Saudiyya don aikin Hajjin bana.

Sai dai hukumar, cikin wata sanarwa da Shafii Sani-Mohammed ya sanya wa hannu, jami’in yada labarai a hukumar, ta musanta aikata duk wani ba daidai ba da ake zargi, tana mai jaddada cewa ana gudanar da aikin ne karkashin wani kwamiti na musamman wanda manyan jagororinsa suka fito daga kwararri a fannin lafiya, ba na hukumar NAHCON ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara