DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kada ku daka ta masu suka, ku yi aikin hidimtawa jama’arku kawai – Sakon Tinubu ga Gwamnonin Nijeriya

-

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bukaci gwamnonin Najeriya da su mai da hankali kan ci gaban al’umma duk da sukar da ake musu, ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kai ziyarar aiki Jihar Katsina, inda ya kaddamar da titin Eastern Bypass mai nisan kilomita 24 da kuma Cibiyar Inganta Noma ta jihar da aka gina a karkashin Gwamna Dikko Radda.

Tinubu ya yaba da jajircewar Gwamna Radda a fannonin noma, lafiya, ilimi da gine-gine, duk da barazanar tsaro da jihar ke fuskantar, inda ya ce gwamnati za ta ci gaba da goyon bayan kokarin jihar wajen tabbatar da zaman lafiya da ci gaba.

Shugaban ya bayyana cewa yunwa da talauci na ci gaba da zama barazana ga zaman lafiya, kuma gwamnatin sa na aiki tukuru wajen tabbatar da wadatar abinci ta hanyar bunkasa noman zamani da inganta tsarin ruwa.

A karshe, Tinubu ya sanar da cewa ana farfado da Bankin Noma domin bai wa manoma rance cikin sauki. Ya kuma bukaci sauran gwamnonin Najeriya su dauki darasi daga tsarin da Katsina take bi wajen yaki da talauci da yunwa a kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara