Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bukaci gwamnonin Najeriya da su mai da hankali kan ci gaban al’umma duk da sukar da ake musu, ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kai ziyarar aiki Jihar Katsina, inda ya kaddamar da titin Eastern Bypass mai nisan kilomita 24 da kuma Cibiyar Inganta Noma ta jihar da aka gina a karkashin Gwamna Dikko Radda.
Tinubu ya yaba da jajircewar Gwamna Radda a fannonin noma, lafiya, ilimi da gine-gine, duk da barazanar tsaro da jihar ke fuskantar, inda ya ce gwamnati za ta ci gaba da goyon bayan kokarin jihar wajen tabbatar da zaman lafiya da ci gaba.
Shugaban ya bayyana cewa yunwa da talauci na ci gaba da zama barazana ga zaman lafiya, kuma gwamnatin sa na aiki tukuru wajen tabbatar da wadatar abinci ta hanyar bunkasa noman zamani da inganta tsarin ruwa.
A karshe, Tinubu ya sanar da cewa ana farfado da Bankin Noma domin bai wa manoma rance cikin sauki. Ya kuma bukaci sauran gwamnonin Najeriya su dauki darasi daga tsarin da Katsina take bi wajen yaki da talauci da yunwa a kasa.