DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar FCCPC ta ce barazanar Meta na ficewa daga Najeriya ba zai hanata zartar da hukuncin ba- Channels TV

-

Hukumar kare hakkin mai Saye da Ingancin fasaha (FCCPC) ta bayyana cewa barazanar kamfanin Meta na ficewa daga Najeriya ba ta hana su bin doka ko janye hukuncin da aka yanke masa ba.

A sanarwa da darektan hulda da jama’a na hukumar, Mista Ondaje Ijagwu, ya fitar a ranar Asabar, hukumar ta zargi~ Meta – wadda ke da mallakar WhatsApp, Facebook da Instagram – da kokarin neman tausayin jama’a da neman rage matsin lambar hukuncin da ake nufin dauka a kansa.

Tun a ranar 19 ga Yuli, 2024, FCCPC ta ci tarar Meta dalar Amurka miliyan 220 bisa take hakkin masu amfani da bayanansu na sirri, tare da karya dokar Federal Competition and Consumer Protection Act (FCCPA) da kuma Nigeria Data Protection Regulation (NDPR).

Rahoton binciken ya tabbatar da cewa Meta da WhatsApp – wadanda aka kira da “Meta Parties” – sun aikata abubuwa da dama da suka sabawa doka. Wadannan suka hada da: hukuncin kotun kare hakkin fasaha da ta ci tarar kamfanin $220m da FCCPC ta kakabawa Meta.

A cewar FCCPC, Meta ta taba fuskantar irin wannan hukunci a wasu kasashen duniya kamar Amurka ($1.5bn a Texas), Tarayyar Turai ($1.3bn), da kuma kasashe kamar India, Faransa, Koriya ta Kudu da Ostiraliya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara