DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Jigawa ya yi girgiza a majalisar kwamishinoninsa

-

Gwamnatin Jihar Jigawa ta sanar da sauye-sauyen mukamai a cikin Majalisar Zartaswa ta jiha, a wani yunkuri na inganta aiki da daidaita tsarin mulki.

A cikin sanarwar da Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu, Sagir Musa Ahmed, ya fitar ya bayyana cewa:

– Hon. Muhammed Alhassan, da ya kasance Kwamishinan Ma’aikatar Gidaje, An mayar da shi zuwa Ma’aikatar Ruwa.

– Hon. Ibrahim Garba Hannun Giwa, da yake Kwamishinan Ruwa, yanzu zai jagoranci Ma’aikatar Kananan Hukumomi da Ci gaban Al’umma.

– Hon. Ahmed Garba (MK), wanda ya ke Kwamishinan Kananan Hukumomi, an tura shi zuwa Ma’aikatar Gidaje, Tsare-Tsaren Birane da Cigaban Yankuna.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa wadannan sauye-sauyen sun fara aiki daga wannan Litinin din, 5 ga Mayu, 2025, kuma an umurci dukkan kwamishinonin da su karɓi sabbin ofisoshinsu kafin Litinin, 19 ga Mayu, 2025.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara