Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya bayyana shirin rufe sansanin ‘yan gudun hijira da ke Muna a Maiduguri cikin makonni masu zuwa.
Gwamnan ya bayyana haka ne a wata ziyarar da ya kai sansanin ranar Litinin.
Zulum ya ce matakin na daga cikin kudurin gwamnatin jihar na rufe dukkanin sansanonin ‘yan gudun hijira dake Maiduguri da sauran wurare.
Kamfanin dillancin labaran Nijeriya NAN ya ruwaito cewa sansanin Muna an kafashi ne biyo bayan tsananin bukatar agaji a jihar kuma a halin yanzu yana dauke da ‘yan gudun hijira kimanin 10,000.
Gwamnan, ya bayyana cewa, aka mayar da kusan kashi 75 cikin dari na ‘yan gudun hijirar zuwa muhallansu, ya kuma tabbatar da cewa gwamnati za ta ba da tallafi don inganta rayuwar sauran ‘yan gudun hijarar yayin da suke shirin komawa gidajensu.