DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu zai gana da kamfanonin samar da lantarki kan bashin Tiriliyan 4 da suke bin gwamnati

-

Shugaba Bola Tinubu zai gana da shugabannin kamfanonin dake samar da wutar lantarki a Nijeriya, a kokarin ganin an biya bashin Naira Tiriliyan 4 da ke barazanar gurgunta hanyoyin samar da wutar lantarki a kasar.

A cewar wata sanarwa da ma’aikatar lantarki ta Nijeriya ta fitar, matakin ya biyo bayan wani taro da aka yi a ranar Talatar da ta gabata tsakanin ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu, da shugabannin kamfanonin a Abuja, a dai dai lokacin da ake ci gaba da fargabar yiwuwar rugujewar tsarin samar da wutar lantarkin a Nijeriya.

Gwamnatin tarayya ta yi alkawarin daukar matakin gaggawa don rage yawan bashin Tiriliyan 4 da ake bi.

Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa kamfanonin sun yi gargadin ga gwamnatin tarayya kan ci gaba da tara bashin da ya haura Tiriliyan 4.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara