Bankin Duniya ya nuna damuwa kan karuwar talauci a Nijeriya, inda ya ce kashi 75.5 na mazauna karkara suna rayuwa a kangin talauci.
Bankin Duniya ya bayyana hakan ne a cikin sabon rahoto na baya-bayan nan na watan Afrilun 2025.
A cikin wani rahoton da kafar Africa’s Pulse ta fitar, biyo bayan taron asusun ba da lamuni na duniya IMF da bankin duniya da ya gudana a Amurka, ta bayyana da dama daga cikin ‘yan Nijeriya za su fada cikin talauci a cikin shekaru biyar masu zuwa.
Rahoton na Bankin Duniya ya bayyana mummunan halin da ake ciki na talauci a kasar, sakamakon tabarbarewar tattalin arziki da rashin daidaito tsakanin mazauna karkara.