DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ana zargin wani matashi ya yi ajalin mahaifinsa a Jigawa

-

Rundunar ‘yan sanda ta kama wani matashi dan shekara 20 mai suna Muhammad Salisu da ake zargin ya yi ajalin mahaifinsa Salisu Abubakar inda ya daddatsa shi da adda a karamar hukumar Gwaram ta jihar Jigawa.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a Dutse, a ranar Litinin, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Shi’isu Adam, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 10 na safe a unguwar Bakin Kasuwa da ke yankin Sara.

A cewar kakakin, wanda ake zargin ya yi amfani da adda, inda ya yi wa mahaifinsa munanan raunuka a kafada, wuyansa, da kuma kirji.

Nan take aka garzaya da shi babban asibiti da ke Birnin Kudu, sai dai a can ne Likita ya tabbatar da mutuwarsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara