By Salim Muhammad Ghali
Hukumar jin daɗin alhazai ta jihar Kaduna ta bayyana cewa za ta fara jigilar maniyata hajjin bana zuwa ƙasar Saudiyya daga ranar 14 ga watan Mayu.
Shugaban hukumar, Malam Salihu S. Abubakar, ne ya bayyana hakan a cikin wani shirin radiyo a yau Talata, inda ya yi bayanin shirye-shiryen da suka yi na gudanar da aikin Hajjin bana.
Kamfanin UMZA Airline ne zai yi jigilar jimillar mahajjata 4,060 na Jihar Kaduna ne ake sa ran za su sauke farali a bana.
Jaridar daily trust ta ruwaito daga cikin matakan da hukumar dauka ta ce dole ne a bi kafin tafiya, an shirya yi wa dukkan mahajjatan binciken lafiya a sansanin mahajjata na Hajj Transit Camp da ke Mando.
Malam Salihu ya ja hankalin dukkan mahajjata da su kiyaye doka da ƙa’idojin da hukumomin Saudiyya suka shimfiɗa, yana mai jaddada muhimmancin ladabi, da biyayya, da kuma kula da lafiya a tsawon lokacin aikin hajji.