Majalisar zartaswa ta Nijeriya ta amince da kashe naira biliyan 750 domin yin sabbin tituna da kuma gyara wasu a jihohin kasar.
Ministan ayyuka, Dave Umahi ne ya bayyana haka ga manema labarai na fadar shugaban kasa a ranar Litinin, bayan taron majalisar da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta.
Umahi ya ce majalisar ta amince da sake yin wasu ayyukan da tsohuwar gwamnatin ba ta kammala ba.
Daga cikin muhimman abubuwan da aka amince da su har da sake aikin hanyar Akure-Eta-Ogbese-Ekiti zuwa Ikere-Ado-Ekiti, wanda ya ratsa jihohin Ondo da Ekiti.
Kazalika majalisar zartaswar ta sake tantance kwangilolin da aka gada a gwamnatocin baya, ta kuma sake duba aikin hanyar Sokoto-Zamfara-Katsina-Kaduna.