DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Bayan zargin jami’an tsaro da tallata laifi, gwamna Zulum ya haramta cinikin giya a Borno

-

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayar da umarnin dakatar da sayar da giya da sauran kayan maye a cikin birnin Maiduguri da kewaye, yana mai zargin wasu jami’an tsaro da hannu a yaduwar laifuka da dabi’un banza a tsakanin al’umma.

Farfesa Zulum ya bayyana haka ne a ranar Talata, yayin kaddamar da kwamitin da aka sake wa fasali domin rushe otal-otal da gidajen karuwai da maboyar ’yan daba da masu aikata laifuka a fadar gwamnatin jihar da ke Maiduguri.

A cewar gwamnan, wasu tsofaffi da ma’aikatan jami’an tsaron da ke aiki a yanzu sun taka rawa matuka wajen jefa matasa cikin ayyukan laifi, irin su ta’addanci, karuwanci, shaye-shaye da kuma dabanci.

Gwamna Zulum ya ce yawaitar sayar da giya da kayan maye na kara haddasa rikici tsakanin kungiyoyin masu tayar da hankali, kawalci, da kuma satar mutane, wanda hakan ke kara barazana ga zaman lafiya da tsaron jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara