DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar tarayya na shirin kafa wani kwamitin sulhu mai ƙarfi da zai shiga tsakani don warware rikicin siyasa a Jihar Rivers.

-

Shugaban majalisar wakilai, honarabul Abbas Tajudeen, ne ya bayyana hakan a ranar Talata, yayin da majalisar ta koma bakin aiki, bayan hutun bukukuwan Easter da Sallah.

Rikicin ya samo asali ne tsakanin Gwamnan Jihar Rivers da aka dakatar, Siminalayi Fubara, da tsohon ubangidansa a siyasa, kuma ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike.

Abbas ya ce kwamitin da za a kafa tare da hadin gwiwar Majalisar Dattawa zai kunshi manyan ‘yan kasa masu kima da mutunci, wadanda za su jagoranci tattaunawa, su samar da zaman lafiya tare da dawo da tsarin dimokiradiyya a Jihar Rivers da sauran jihohin da ke fuskantar rikice-rikice irin wannan.

Shugaban masu rinjaye a Majalisar Dattawa, Sanata Opeyemi Bamidele, shi ne zai shugabanci kwamitin sulhun. Daga cikin mambobin kwamitin akwai Sanata Adamu Aliero daga Jihar Kebbi, Sanata Osita Izunaso daga Imo, Sanata Osita Ngwu daga Enugu, Sanata Kaka Shehu daga Borno, Sanata Aminu Abass daga Adamawa, Sanata Tokunbo Abiru daga Legas, da Sanata Adeniyi Adegbonmire daga Jihar Ondo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara