DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za mu karɓi Kwankwaso idan ya yanke shawarar koma wa APC- Ganduje

-

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa jam’iyyar za ta karɓi tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, idan har ya yanke shawarar dawowa jam’iyyar.

Ganduje ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin da Ministan Jiha na Ma’aikatar Gidaje da Cigaban Birane, Hon. Yusuf Ibrahim Atah, ya kai masa ziyarar ban girma a hedikwatar APC da ke Abuja.

Ya ce, idan mutum yana neman mafaka daga gida guda, wajibi ne a buɗe masa ƙofa, musamman idan akwai dangantaka ta siyasa da tarihi tsakaninsu.

A baya -bayan nan rahotanni sun nuna cewa jam’iyyar APC na ci gaba da karɓar sabbin mambobi daga sauran jam’iyyu, musamman a wasu jahohin da ke fama da rikicin siyasa na cikin gida.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara