DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Bello Turji na cikin matsin lamba daga sojojin Nijeriya – Minista Badaru

-

Ministan Tsaro na Najeriya, Muhammad Badaru, ya bayyana cewa shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji yana gudun hijira sakamakon hare-haren da sojojin Najeriya ke kai wa a ‘yan kwanakin nan.

A cewarsa, rundunar soji ta samu nasarar kashe wasu daga cikin manyan shugabannin ‘yan ta’adda da suka hada da:

Maza Barume Madaro da Kachalla Alhaji Dati da Bani Wala Burki da Kachalla Dogo Kwaden da Chairman Hanazuma sai kuma Kachalla Bandiyo da Maiyara Madaci da sauransu.

Minista Badaru ya ce dakarun soji na ci gaba da murkushe ‘yan ta’adda, kuma yawancin shugabanninsu suna cikin firgici da gudu.

Ya kara da cewa sojoji na kara kaimi wajen tattara bayanan sirri domin hana hare-haren ta’addanci kafin su faru.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara