DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Na bar PDP ne don cigaba da dangwalar arzikin da ke cikin kujerar da nake rike da ita – Shugaban majalisar dokokin jihar Edo

-

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Edo, Rt. Hon. Blessing Agbebaku, ya bayyana dalilin da ya sa ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC.

Agbebaku, tare da wasu ‘yan majalisa biyu — Hon. Sunday Fada Eigbiremonlen da Hon. Idaiye Yekini Oisayemoje — sun sanar da sauya shekar su zuwa jam’iyyar APC a ranar Talata.

A yayin da yake sanar da wannan mataki a zauren majalisar a ranar Laraba, Agbebaku ya ce sauya shekar tasa ya samo asali ne daga niyyarsa ta ci gaba da rike kujerar shugaban majalisa domin amfanin mazabarsa.

Shugaban majalisar ya jaddada cewa sauya shekar ba don wani amfani na kai ba ne, illa dai kishin ci gaban al’umma da yankin da ya fito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara