DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan majalisa uku daga jihar Katsina sun bar PDP sun koma APC

-

‘Yan majalisar wakila uku daga jihar Katsina sun bar jam’iyyarsu ta PDP sun koma APC.

‘Yan majalisar su ne Ali Iliyasu na Safana/Batsari/Danmusa, Salisu Yusuf Majigiri na Mashi/Dutsi da Abdullahi Balarabe na Bakori/Danja.

Kakakin majalisar wakilan Tajuddeen Abbas ne ya karanta sanarwar ficewar ta su.

‘Yan majalisar dai sun bayyana rikicin da ya addabi jam’iyyar PDP ne ya sa suka bar ta. Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ya ziyarci majalisar don gane wa idonsa yadda ‘yan majalisar suka sauya sheka suka koma jam’iyya mai mulki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara