DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sanda sun kama mutumin da ya nada kansa Dagacin kauye a jihar Ondo

-

‘Yan sanda a jihar Ondo sun tabbatar da cafke wani mutum da ya bayyana kansa a matsayin Basaraken gargajiya, Adekolajo Aladeseyi, bisa zargin nada kansa a matsayin Olujare na Ijare da ke karamar hukumar Ifedore ta jihar.

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya NAN ya rawaito cewa an kama karin wasu mutane hudu da ake zargin sun taimaka masa wajen gudanar da nadin.

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Olutokunbo Afolabi, yayin da yake tabbatar da kama Aladeseyi, ya ce an cafke shi ne bisa umurnin gwamnatin jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara