DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba gasa muke yi da kamfanin NNPCL ba – Dangote

-

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, alhaji Aliko Dangote, ya bayyana cewa matatar man fetur dinsa ba ta yin gasa da Kamfanin man Fetur na Nijeriya, wato NNPC.

Dangote ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin wata ziyarar ban girma da ya kai wa sabon shugaban rukunin NNPC, Injiniya Bayo Ojulari, a hedkwatar kamfanin da ke Abuja.

A wata sanarwa da mai magana da yawun NNPC, Olufemi Soneye, ya fitar a yau Jumma’a, Dangote ya ce akwai bukatar haɗin gwiwa domin tabbatar da samar da makamashi mai ɗorewa a ƙasar nan.

Ziyarar, a cewar Soneye, na cikin matakan da ake ɗauka domin ƙarfafa dangantaka da fahimtar juna tsakanin manyan kamfanonin mai biyu—na gwamnati da na masu zaman kansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara