DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Cin hanci la’ana ce, mu tsabtace kanmu daga rashawa- EFCC

-

A wani sakon tunatarwa da ta wallafa a shafinta na Facebook albarkacin ranar Juma’a, hukumar da ke yaĆ™i da cin hanci da rashawa a Najeriya, wato EFCC, ta bayyana cewa cin hanci wata la’ana ce da ke lalata al’umma, tana mai kira ga ‘yan Najeriya da su tsabtace kansu daga wannan mummunar dabi’a.

EFCC ta ambaci wani hadisi daga cikin Sahih Hadith ɗin Abu Dawud mai lamba ta 3580, inda Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Allah ya la’anci mai bayar da cin hanci da wanda aka baiwa.”

Hukumar ta ce, kowane ɗan ƙasa na da rawar da zai taka wajen yaƙar cin hanci da gina ƙasa mai gaskiya da adalci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara