A ranar Juma’a, 9 ga Mayu, 2025, fadar gwamatin ta Jamhuriyar Nijar ta karɓi sabbin jakadun daga jakadun ƙasashen duniya guda takwas.
Inda shugaban mulkin sojin kasar, Janar Abdurahamane Tiani, ya jagoranci wata muhimmiyar liyafa ta diflomasiyya.
Jakadun da suka miƙa takardunsu ga shugaban Ƙasar sun haɗa da:
Maidame Kathleen Fitzgibbon daga Amurka da Ali Tiztak daga Iran da Sir Alex Owiredu Adu daga Ghana da Sir Sita Ram Meena daga India.
Sauran su ne Dr. Oliver Schnakenberg daga Jamhuriyar Tarayyar Jamus da Dr. Ibrahim Awad Ahmed Mohamed Baroudi daga Sudan da Mr. Abdou Diallo daga Burkina Faso da Monsieur José Julián Cala Sagüe daga Jamhuriyar Cuba.