DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilan Nijeriya ta ba gwamnonin Benue da Zamfara da shugabannin majalisunsu su wa’adin mako daya su gaggauta bayyana a gaban kwamitinta

-

Majalisar wakilan Nijeriya ta ba gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia, da na jihar Zamfara, Dauda Lawal, tare da shugabannin majalisun dokokin jihunsu wa’adin mako guda domin su bayyana a gaban kwamitin majalisar kan korafe-korafen da jama’a a kansu.

Wannan umarni ya biyo bayan gaza halartar zaman sauraron koke-koke da aka gudanar a ranar Alhamis da ta gabata a zauren majalisar da ke Abuja, duk da gayyatar da aka riga aka aikewa Gwamnonin.

Wannan korafi dai ya samo asali ne daga wani kudiri da Mataimakin Kakakin Yada Labarai na Majalisar Wakilai, Hon. Philip Agbese, ya gabatar a gaban zauren majalisar a ranar 27 ga Maris.

A zaman farko na kwamitin da aka gudanar ranar Alhamis, Hon. Douglas Akya daga mazabar Makurdi ta Kudu ya jagoranci tawagar ‘yan majalisar da aka dakatar daga Jihar Benue, yayin da Hon. Aliyu Ango Kagara daga Talata Mafara ta kudu tare da Shugaban ‘Yan adawa na Majalisar Zamfara suka wakilci ‘yan uwansu da abin ya shafa.

Kwamitin ya jaddada muhimmancin bayyanar dukkan wadanda aka gayyata, tare da bayyana cewa rashin halarta na gaba na iya fassaruwa a matsayin raini ga majalisar da kuma shari’ar da ke gaban ta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara